Jam’iyyar APC a nan Kano ta bukaci a gaggauta dauke shugaban hukumar zabe na Kano Amb, Abdu Zango zuwa wata jihar.
Shugaban jam’iyyar APC na Kano Abdullahi Abbas ne yayi wanna kira yayin zanga-zangar da suka gudanar ranar Laraba.
Ya kuma bukaci a gudanar da bincike na musamman kan dalilan da suka Sanya INEC ta bayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Kano.
Idan za a iya tunawa a ranar Litinin din da ta gabata ne INEC ta bayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin Wanda ya lashe zaben Kano.
Wanna ce ma ta Sanya jam’iyyar ta APC ta gudanar da zanga zangar adawa da sakamakon.