Majalisar dokokin Kano ta amince da dokar kula da mata masu juna biyu da kananan yara kyauta a asibitocin jihar Kano.
Wannan ya biyo bayan tsallake karatu na uku da dokar tayi yayin zaman majalisar a Larabar nan karkashin shugaban ta Injiniya Hamisu Ibrahim Chidari.
Dokar dai zata bada damar kulawa da mata masu juna biyu da jarirai kyauta a asibitocin jihar Kano.
A dai zaman, majalisar ta amince da karatu na biyu na kudirin dokar hukumar samar da tituna a karkara ta jihar Kano.
Da yake jawabi a zauren majalisar shugaban masu rinjaye Labaran Abdul Madari, ya ce samar da hukumar zai taimaka wajen gina hanyoyi da tituna a karkara domin cigaban su.
Ya ce hukumar samar da titunan zata taimaka wajen bunkasa harkokin noma da kasuwanci a karkara da kuma ingantuwar tsaro.
Majalisar ta amince da karatu na biyu na gyaran dokar hukumar taimakekeniya a harkar lafiya ta jihar Kano.