Saurari premier Radio
39.9 C
Kano
Monday, May 20, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiNAHCON ta sanya ranar fara jigilar maniyyatan hajjin bana zuwa kasa mai...

NAHCON ta sanya ranar fara jigilar maniyyatan hajjin bana zuwa kasa mai tsarki

Date:

Hukumar kula da aikin Hajji ta kasa NAHCON ta ce babu wata jiha da take da damar kara kudin kujerar aikin hajjin bana.

Shugaban hukumar Alhazai na kasa Alhaji Zikrullah Hassan ne ya bayyana haka a wajen taron shugabannin hukumar Alhazai na jihohi da sauran hukumomi.

Ya ce duka hukumomin alhazai jihohin kasar nan 36 sun amince da kudin kujerar aikin hajji da hukumar ta sanar.

Ya kara da cewa hukumar ta amince cewa za a fara jigilar maniyyata ranar 21 ga watan Mayun gobe.

Zikrullah Hassan ya ce hukumar Alhazan za ta sake nazarin kujerun da ta warewa kowacce jiha tare da masu ruwa da tsaki a gobe Juma’a.

Latest stories

Gwamnan Katsina ya nemi tallafi kan karancin abinci da matsalar tsaro ta haddasa.

A wani alk’amarin kuma, Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda,...

Related stories

Gwamnan Katsina ya nemi tallafi kan karancin abinci da matsalar tsaro ta haddasa.

A wani alk’amarin kuma, Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda,...