Saurari premier Radio
40.9 C
Kano
Saturday, May 18, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiYan bindiga sun saki tsohon mataimakin gwamnan jihar Nassarawa

Yan bindiga sun saki tsohon mataimakin gwamnan jihar Nassarawa

Date:

Karibullah Abdulhamid Namadobi

An sako tsohon mataimakin gwamnan jihar Nassarawa Farfesa Onje Gye-Wado da wasu ‘yan bindiga suka sace ranar 7 ga watan Afrilu.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar DSP Ramhan Nansel ne ya tabbatar da hakan ga kamfanin dillancin labarai na kasa NAN a yau Litinin.

DSP Ramhan Nansel ya ce tsohon mataimakin gwamnan ya samu iskar yanci ne da misalin karfe 9:00 na daren ranar Lahadi data gabata, kuma ya sake haduwa da iyalansa.

Ya kara da cewa ‘yan sandan ba su da masaniyar wani kudin fansa da aka biya kafin a sako shi.

A cewarsa, an saki shine ne saboda matsin lamba da hadin gwiwar jami’an tsaro suka yi wa masu garkuwa da mutanen.

Latest stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...

Related stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...