Saurari premier Radio
27.9 C
Kano
Thursday, May 2, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiSojoji sun kashe Ali Dogo da wasu mutum 30

Sojoji sun kashe Ali Dogo da wasu mutum 30

Date:

Sojojin Saman Najeriya sun samu nasarar kashe kasurgumin dan fashin dajin nan da ya addabi Jihar Kaduna, Ali Dogo, tare da wasu mutanensa 30.

Rahotanni sun ce sojojin ‘Operation WHIRL Punch’ sun fattaki Dogo, wanda aka fi sani da Yellow da mayakansa ne a karshen makon da ya gabata.

Sojojin sun yi wa Yellow da mayakan nasa dirar mikiya ne a daidai lokacin da suke tsaka da tattaunawa a gidan Alhaji Gwarzo, inda jirgin yakin ya sakar wa ginin wuta ya hallaka su baki daya.

Kazalika, sojojin sun sake kai samame kan ‘yan bindiga a yankin Mando da ke Arewa maso Yammacin Kaduna.

Bayanai sun ce sojoji sun kai samamen ne bayan tattara bayanan sirrin da suka samu game da shirin ‘yan bindigar da kuma inda suke.

An ji mai magana da yawun rundunar sojojin sama, AC Edward Gabkwet, ya tabbatar da nasarorin da suka samu.

Haka nan, ya ce ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen ci gaba da fatattakar ‘yan ta’adda da harkokinsu a shiyyar Arewa maso Yamma.

Latest stories

Netanyahu ya nanata ƙudirin sojojin Isra’ila na kai farmaki ta ƙasa a Rafah.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya nanata kudirin sojojin Isra'ila...

NiMet ta yi hasashen samun mamakon ruwan sama a wasu jihohin.

Wani has ashen hukumar Kula da Yanayi ta kasa...

Related stories

Netanyahu ya nanata ƙudirin sojojin Isra’ila na kai farmaki ta ƙasa a Rafah.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya nanata kudirin sojojin Isra'ila...

NiMet ta yi hasashen samun mamakon ruwan sama a wasu jihohin.

Wani has ashen hukumar Kula da Yanayi ta kasa...