A yau larabar nan shugaban kasar nan Muhammadu Buhari ya rantsar da sabon Alkalin Alkalan kasar nan Mai Shari’a Olukayode Ariwoola a babban birnin taryya Abuja.
Wannan na zuwa ne bayan da ya shafe watanni hudu yana rikon kwarya biyo bayan murabus din da Mai shari’a Ibrahim Tanko yayi.
A wani sako da fadar shugaban kasar ta wallafa a shafin Tuwita ya nuna cewa Alkalin Alkalan Najeriyar ya karbi rantsuwar fara aikin ne da safiyar yau Laraba.
An haife Mai Shari’a Olukayode Ariwoola a watan Agustan shekarar 1954 a Jihar Oyo, kuma ya yi alkalanci a Kotun Daukaka Kara ta kasar nan, kafin ya samu karin matsayi zuwa Kotun Koli.