Saurari premier Radio
37.9 C
Kano
Friday, April 26, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiBuhari ya  rantsar da sabon Alkalin Alkalai na kasa

Buhari ya  rantsar da sabon Alkalin Alkalai na kasa

Date:

A yau larabar nan shugaban kasar nan Muhammadu Buhari ya rantsar da sabon  Alkalin Alkalan kasar nan  Mai Shari’a Olukayode Ariwoola a babban birnin taryya Abuja.

Wannan na zuwa ne bayan da ya shafe watanni hudu yana rikon kwarya biyo bayan murabus din da Mai shari’a Ibrahim Tanko yayi.

A wani sako da fadar shugaban kasar ta wallafa a shafin Tuwita ya nuna cewa Alkalin Alkalan Najeriyar ya karbi  rantsuwar fara aikin  ne da safiyar yau Laraba.

An haife Mai Shari’a Olukayode Ariwoola a watan Agustan shekarar 1954 a Jihar Oyo, kuma ya yi alkalanci a Kotun Daukaka Kara ta kasar nan, kafin ya samu karin matsayi zuwa Kotun Koli.

Latest stories

Related stories