Jam’iyyar APC ta ce shugaban kasa Muhammadu Buhari ne zai yanke hukunci kan lokacin da za a fara yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar.
Mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasar Mr Festus Keyamo ne ya bayyana haka bayan kammala taron da shugabannin jam’iyyar suka gudanar tare da gwamnoni da kuma kwamitin yakin neman zaben a ranar Laraba a Abuja.
Jam’iyyar dai ta yi ta sake ranakun game da ranar kaddamar da yakin neman zaben shugaban kasar, sakamakon rikice-rikice da suka dabaibaye jam’iyyar da mutanen da ke cikin kwamitin yakin neman zaben.
Keyamo ya kuma kara da cewa kawunan ƴaƴan jam’iyyar a hade suke kuma jam’iyyar suce zata samu nasarra a babban zaben da zaa gudanar a shekara mai zuwa.