Saurari premier Radio
28.9 C
Kano
Friday, May 3, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiNIMET ta yi hasashen samun ruwan sama da iska mai karfi a...

NIMET ta yi hasashen samun ruwan sama da iska mai karfi a arewacin kasar nan

Date:

Abdurrashid Hussain

Hukumar kula da yanayi ta kasa NIMET ta yi hasashen samun yanayin hadari da ruwan sama daga ranar Litinin zuwa Laraba.

Sakamakon hasashen yanayin da NIMET ta fitar a Abuja ya nuna cewa za a yi ruwan sama kamar da bakin kwarya da sanyin safiya a Jihohin Sokoto, Zamfara, Kebbi da Katsina.

Za kuma a samu ruwan da rana a wasu sassan Bauchi, Kaduna da Taraba.

NIMET ta kuma yi hasashen cewa sararin samaniya a ranar Talata zai kasance cikin yanayin hasken rana jefi-jefi a yankin arewacin kasar nan da yiwuwar samun tsawa a sassan jihar Taraba da safe.

Yayin da ake sa ran samun tsawa a wasu sassan jihohin Kebbi, Zamfara, Sokoto, Kaduna, Kano, Borno, Gombe, Adamawa da Taraba da yammacin ranar.

Latest stories

Related stories