Saurari premier Radio
26.3 C
Kano
Sunday, May 5, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiAddiniAn nada Sheikh Nuru Khalid sabon limamin Juma'a a Abuja

An nada Sheikh Nuru Khalid sabon limamin Juma’a a Abuja

Date:

Mukhtar Yahya Usman
Sabon Masallacin Juma’a da ke unguwar bayan babban bankin kasa CBN ya nada sheikh Nuru Khalid babban limamin Masallacin.

Wannan na zuwa ne awannin kadan bayan da kwamitin Masallacin Juma’a na APO ya Kori Malamin baki daya.

Kwamitin Masallacin ya zargi Malamin da gudanar da hudubar da za ta tada hankulan jama’a.

A cewar shugaban kwamitin Masallacin Sanata Dan Sadau, sun kori Malamin ne saboda kin nuna nadamarsa bayan da aka dakatar da shi.

Sai dai jim kadan bayan korar tasa ne malamin ya samu sabon aiki da Masallacin da ke unguwar babban bankin kasa CBN.

Ana sa ran zai kama aiki a ranar Juma’a mai zuwa 8 ga Aprilu, Inda zai jagoranco Sallar Juma’a.

Latest stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Related stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...