Saurari premier Radio
27.9 C
Kano
Sunday, May 19, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiAna fargabar hadarin mota ya kashe mutum 11 a Kano

Ana fargabar hadarin mota ya kashe mutum 11 a Kano

Date:

Mukhtar Yahya Usman

Ana fargabar mutuwar mutane 11 wasu hudu suka jikkata a wani mummunan hadarin mota da ya afku a garin Tsamiya da ke karamar hukumar Kura a nan Kano.

Shaidun gani da ido sunce hadarin ya faru ne da misalign karfe 3:30 na yammacin yau Litinin.

A cewarsu wata motar dakon kaya ta kamfanin Dangote ce ta haddasa hadarin.

Wani shaidar gani da ido Umar Sani ya ce motoci ne biyu kirar Hayis da J5 suka yi taho mu gama.

Ya ce motar Dangoten ce ke gudun wuce sa’a ta dannesu lokacin da take kokarin wucewa da gaggawa.

Har yanzu ana ci gaba da zakulo wadanda suka mutu da wadanda suka yi rauni a cikin motocin.

Muntuntubi jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta Jihar Kano ba mu sameshi ba amma dai za mu ci gaba da bibiyarsa.

Latest stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...

Related stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...