Kungiyar dattawan Arewa ta musanta labarin da ke yawo cewa ta zabi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar a matsayin dan takarar da take goyon baya.
Wani mamba a kungiyar Alhaji Seidu Baba, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a Abuja.
Ya ce kungiyar ba ta amince da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar matsayin dan takarar da yafi kowa cancanta ba.
Alhaji Seidu Baba ya bukaci al’ummar arewacin Najeriya su yi watsi da duk wani shiri na ganin an tilasta musu zaben wani dan takara.