Shugaban kasa Bola Tinubu ya dawo gida Najeriya daga ziyarar da kai Turai a yau Laraba.
Shugaban ya samu tarba daga mamnyan mukarraban gwamnati a fadar Villa kamar yadda gidan Talabijin na kasa NTA ya bayyana.
Dama a jiya Talata, mai taimakawa shugabnan kasar kan yada labarai Bayo Onanuga ya sanar a shafin sa nma X cewar shugaba Tinubu zai dawo gida a yau Laraba.
A ranar 22 ga Afrilu ne, Tinubu ya bar Abuja, babban birnin kasar, zuwa Masarautar Netherlands a wata ziyarar aiki.
Wata sanrwa ma daga Ajuri Ngelale, mai magana da yawun shugaban kasar ya ce shugaban ya ziyarci kasar Netherland ne bisa gayyatar da firaminista Mark Rutte ya yi masa.
Bayan Netherlands, Tinubu ya wuce zuwa birnin Riyadh na kasar Saudiyya domin halartar wani taro na musamman na dandalin tattalin arzikin duniya tsakanin 28 da 29 ga Afrilu.