Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya sauka birnin Riyadh dake Saudiyya.
Tinubu ya Isa Saudiyya, gabanin taron da ƙasar ta shirya da kasashen Afirka.
Tinubu ya samu tarba daga mataimakin gwamnan Riyadh, Mohammed bin Abdulrahman Abdulaziz da kuma ambasadan Najeriya a Saudiyya, Yahaya Lawal.
Shugaban na Najeriya ya sauka a filin jirgin sama na King Khalid Airport dake Riyadh.