Hukumar zabe ta kasa INEC, ta ce matsalar tsaro ne dalilin da ya janyo karancin masu fitowa karbar katin zabe a jihar Katsina.
Kwamishinan hukumar a jihar Katsina Jibrin Zarewa ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai a jihar.
Yace ba ko wanne yanki hukumar ke iya tura jami’an ta, don yiwa mutane rijistar katin zaben ba.
A cewa sa suna fargabar matsalar zata iya shafar jami’an nasu.
Ya ce a yanzu haka cibiyoyin da suke bada katin ma akwai karancin fitowar mutane saboda tsoro.
Jihar Katsina dai na daga cikin jihohin da hukumar zaben ta kasa ta bayyana, a matsayin wadda aka samu karancin masu fitowa karbar katin zabe, duk da kasancewar ta ta hudu a yawan al’umma a kasar nan.