Saurari premier Radio
24.5 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiRashin tsaro ya janyo karancin masu karbar katin zabe a Katsina-INEC

Rashin tsaro ya janyo karancin masu karbar katin zabe a Katsina-INEC

Date:

Hukumar zabe ta kasa INEC, ta ce matsalar tsaro ne dalilin da ya janyo karancin masu fitowa karbar katin zabe a jihar Katsina.

Kwamishinan hukumar a jihar Katsina Jibrin Zarewa ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai a jihar.

Yace ba ko wanne yanki hukumar ke iya tura jamiā€™an ta, don yiwa mutane rijistar katin zaben ba.

A cewa sa suna fargabar matsalar zata iya shafar jamiā€™an nasu.

Ya ce a yanzu haka cibiyoyin da suke bada katin ma akwai karancin fitowar mutane saboda tsoro.

Jihar Katsina dai na daga cikin jihohin da hukumar zaben ta kasa ta bayyana, a matsayin wadda aka samu karancin masu fitowa karbar katin zabe, duk da kasancewar ta ta hudu a yawan alā€™umma a kasar nan.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...