Saurari premier Radio
34.9 C
Kano
Friday, April 26, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiKasuwanciNCAA Ta Janye Dakatarwar Kamfanin Azman

NCAA Ta Janye Dakatarwar Kamfanin Azman

Date:

Abdurashi Hussain

Kamfanin jiragen sama na Azman ya sanar da dawowa zirga-zirgar jiragensa bayan dakatarwar da hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta kasa ta yi masa.

 

Babban daraktan hukumar, Kyaftin Musa Nuhu ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a birnin Ikko.

 

Hukumar ta dakatar da kamfanin ne saboda gazawarsa wajen biyan Naira miliyan dubu 2 da doriya na tikitin fasinjoji.

 

Kamfanin na Azman ya ce ya tattauna da hukumar a yau wanda hakan ya kai ga dage dakatarwar da aka yi wa kamfanin.

 

Injiniya Nuraddeen Aliyu shine mataimakin babban manajan kamfanin na Azman, da ya shaidawa Premier cewa sun dawo da aiki, kuma yanzu haka dukkan jiragensu za su cigaba da jigila daga yau Juma’a kamar yadda aka tsara.

Latest stories

Related stories