Majalisar wakilai ta ce shugaban kasa Muhammadu Buhari zai gabatar da kasafin kudin badi a makon farko na watan Oktoba.
Kakakin Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila, ya bayyana hakan lokacin da yake yiwa manema Labarai jawabi, jim kadan bayan kammala duba dakunan taron sauraron ra’ayoyin jama’a na 28 da kuma 234 da majalisar za ta yi amfani dasu.
Majalisar za ta yi afani da zaueuka ne na wucin gadi don gudanar da zamanta na yau da kullum, sakamakon gyare-gyaren da ake kan yiwa zauren majilar a halin yanzu.
Yace za’a kammala saita wurin da majalisar za ta rika amfani dashi a matsayin zauren ta na wucin gadi gabanin ranar 20 ga watan da muke ciki, lokacin da majalisar zata koma bakin aiki.
Femi Gbajabiamila ya kara da cewa, aikin gyara majalisar zai fi amfanar sabbin yan majalisa masu zuwa kasancewar ba zai kammala ba har cikin watan Augustan badi.