Gwamnatin tarayya da kasar Birtaniya sun sanya hannu kan wata yarjejeniya domin magance matsalar safarar miyagun kwayoyi a wani bangare na kokarin dakile munanan laifuka a kasashen biyu.
An sanya hannu kan sabuwar yarjejeniyar fahimtar junan a Abuja, tsakanin hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA da ta kula da laifukai ta Birtaniya NCA.
Shugaban NDLEA, Buba Marwa ne ya sanya hannun a madadin gwamnatin tarayya yayin da manajan hukumar kula da laifukan kasa ta Birtaniya a yammacin Afirka, David Cater, ya sanya hannu a madadin Birtaniyar.
Buba Marwa ya ce wannan sabuwar yarjejeniyar za ta haifar da hanyoyin samun bayanai kan masu aikata laifuka ko inda suke boye don fuskantar hukunci.
A nashi jawabin manajan yammacin Afirka a hukumar kula da laifuka ta Birtaniya, David Cater, ya ce an yi yarjejeniyar ne saboda gamsuwa da ayyukan NDLEA.
VON/AH