Saurari premier Radio
32.4 C
Kano
Tuesday, April 30, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiNAHCON ta sanya ranar fara jigilar maniyyatan hajjin bana zuwa kasa mai...

NAHCON ta sanya ranar fara jigilar maniyyatan hajjin bana zuwa kasa mai tsarki

Date:

Hukumar kula da aikin Hajji ta kasa NAHCON ta ce babu wata jiha da take da damar kara kudin kujerar aikin hajjin bana.

Shugaban hukumar Alhazai na kasa Alhaji Zikrullah Hassan ne ya bayyana haka a wajen taron shugabannin hukumar Alhazai na jihohi da sauran hukumomi.

Ya ce duka hukumomin alhazai jihohin kasar nan 36 sun amince da kudin kujerar aikin hajji da hukumar ta sanar.

Ya kara da cewa hukumar ta amince cewa za a fara jigilar maniyyata ranar 21 ga watan Mayun gobe.

Zikrullah Hassan ya ce hukumar Alhazan za ta sake nazarin kujerun da ta warewa kowacce jiha tare da masu ruwa da tsaki a gobe Juma’a.

Latest stories

Ƙungiyar Hamas ta isa birnin Al-Qahira game da tattaunawa kan tsagaita wuta.

Rahotanni daga kasar Masar, sun ce tawagar jami’an kungiyar...

An kashe ƴan ƙato da gora sama da 23 a Barno da Sakkwato.

Rahotanni daga jihohin Borno da Sakkwato sun ce, an...

Related stories

Ƙungiyar Hamas ta isa birnin Al-Qahira game da tattaunawa kan tsagaita wuta.

Rahotanni daga kasar Masar, sun ce tawagar jami’an kungiyar...

An kashe ƴan ƙato da gora sama da 23 a Barno da Sakkwato.

Rahotanni daga jihohin Borno da Sakkwato sun ce, an...