Kungiyar dillalan man fetur ta kasa IPMAN, ta ce za ta sanar da matsayarta kan kudaden dakonsu da gwamnatin tarayya ta rike musu.
Sakataren kudi na kungiyar, Alhaji Musa Yahya Mai Kifi ne ya bayyana hakan a zantawarsa da wakiliyarmu, Hauwa Halliru Gwangwazo.
Mai Kifi ya ce gwamnatin tarayya ta rike wa mambobinta kudin dakonsu da ya haura Naira biliyan 15.
Ya ce saboda haka za su samar da matsaya ta rufe gidajen mansu bayan bukukuwan kirismeti da na sabuwar shekara.
Ko a ranar Alhamis ma, shugaban kungiyar ta IPMAN dake kula da jihohin Anambra, Ebonyi da Enugu, Mr Chinedu Anyaso, ya yi barazanar cewa yayan kungiyar za su tsayar da aiki idan har gwamnatin tarayya bata biyasu hakkokinsu ba.