Gwamnatin tarayya ta shirya tsaf don fara shari’a da wasu yan Bokoharam akalla 2000, da ake zargi da hannu a wanzar da ayyukan ta’addanci daban daban.
Majiyoyi sun shaidawa jaridar Punch cewa an kammala shirin ne tun a gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da ta shude.
Za’a gudanar da shari’ar ce a Kainji dake jihar Niger karkashin tsattsauran tsaro, inda dakarun soji na Operation Safe Corridor ke dabdala.
Wata majiya ta tabbatar da cewa alkalin alkalan kasarnan ya tanadi lauyoyi 8 da zasu fuskanci shari’ar, to sai dai babu masaniyar ko zasu rika bayyana ne a lokacin guda.