Gwamnatin tarayya ta ce za ta kashe sama da Naira miliyan dubu 22 wajen ciyar da daurarru da ke gidajen yarin kasar nan a shekarar 2023.
Babban sakataren ma’aikatar cikin gida, Dr. Shu’aibu Belgore ne ya bayyana haka n yau a Abuja, yayi tarob kwanaki biyu kan yadda za a rage cinkoso a gidajen yarin.
Ya ce kudin na cikin kasafin bana da shugaban kasa ya gabatarwa majalisun tarayya.
Ya ce ana samun karuwar cinkoso a gidajen yarin, kuma kashi 80 na daurarrun na jiran shari’a ne.