Daga Mukhtar Yahaya Usman
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana gwamna Ganduje a matsayin gwamnan da ya mayar da Kano Sabuwa.
Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da jami’in yada labaran Shugaban kasar Malam Garba Shehu ya fitar ranar Lahadi.
Sanarwar dai wani bangare ne na taya gwamnan cika shekaru 73 a duniya.
Ya kuma yabawa gwamnan kan irin rawar da ya taka a bangaren tsaro a jihar Kano.
Buhari ya kuma bukaci gwamnan da ya ci gaba da jajircewa kan ayyukan raya kasa da ya ke gudanarwa a Kano.