Fiye da Falasdinawa 34,900 ne aka kashe tare da jikkata 78,500 tun bayan da Isra’ila ta kaddamar da yakinta na soji a Gaza, in ji ma’aikatar lafiya ta Hamas a yankin.
A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, an kashe mutum 60 tare da raunata 110 in ji ma’aikatar.
Sojojin Isra’ila sun fara wani gagarumin farmakin ramuwar gayya a Gaza bayan da aka kashe kimanin mutum 1,200 tare da yin garkuwa da wasu 252 a harin da Hamas ta kai kan Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoba.