Karibullah Abdulhamid Namadobi
Shugaban kasa Muhammadu Buhari na jagorantar bikin kaddamar da matatar man fetur mafi girma a nahiyar Afirka, Kuma guda cikin manyan matatun Mai a duniya.
Matatar mallakin hamshakin dan kasuwar nan, mafi kudi a Afirka kuma dan asalin Kano, zata na tace danyan mai a wannan kasa.
Matatar man da aka kashe kudin da ya haura Dala biliyan 20 ta shiga sahun manyan matatun Mai a duniya.
Ana ganin samar da matatar zai kawo karshen fitar da danyan mai da Najeriya keyi Don tacewa.
A jawabinshi hamshakin dan kasuwar ya ce wannan bikin kaddamarwa na zama tamkar wata kafa damba don cimma manufar habbaka tattalin arzikin kasar nan.
Matatar dai an ginata ne a jihar Lagas dake Najeriya.