Jam’iyyar APC a Kano ta yi watsi da ikirarin kwamatin karbar mulkin NNPP na shirya zagon kasa ga shirin mika mulki ga sabuwar gwamnati.
Ta ce matakan fidda sanarwa da NNPP ke yi, wuce gona da iri ne ga gwamnatin da kawo yanzu ludayinta ke kan dawo.
Mai magana da yawun jam’iyyar, Ahmad Aruwa ne ya bayyana hakan ga Premier Radio.
Yace a shirye suke tsaf wajen mika mulki a ranar 29 ga watan Mayu, domin tabbatuwar zaman lafiya a jihar Kano.