Saurari premier Radio
26.9 C
Kano
Sunday, May 19, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiDa Dumi-dumiHukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Date:

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki zagon kasa, Ola Olukayide, ya musanta zargin shi ne ya fara bincikar tsohon gwamnan Kogi, Yahya Bello.

A wata hira da manema labarai jiya a Abuja, shugaban na EFCC ya ce shi ma gadar binciken ya yi daga tsohon shugaban hukumar.

Ya kuma ce ba shi da wani dalilin yi wa Yahya Bello bi-ta-da-kulli, illa kishin ganin an samu ci gaba a kasar nan, musamman ganin yadda cikin wata shida da fara aiki a hukumar, aka samu damar kwato kudi naira milyan dubu 120 daga hannun ‘yan damfara.

Mr Olukayide, ya musanta cewa jami’ansu na aiki da son zuciya tun bayan da ya kama aiki a bara, kuma matukar ba su bibiyi shari’ar Yahya Bello ba, EFCC ba za ta iya bincikar kowa ba ke nan.

 

Latest stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...

Related stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...