Wata gobara da ta tashi a Kasuwar Yan Katato da ke karamar hukumar Sabon Garin jihar Kaduna, shaguna 100 da kayayyakin miliyoyin Naira.
Shugaban kasuwar, Mohammed Ashiru, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na kasa NAN a Zariya cewa, gobarar ta tashi ne sakamakon tartsatsin wayar wutar lantarki da ta bi ta kasuwar.
Ya ce jami’ai sun shawo kan gobarar bayan wasu sa’o’i ta na ci, in da ya jajantawa masu shagunan da abin ya shafa.
Jami’in hukumar kashe gobara ta tarayya, Abubakar Ibrahim, ya ce rashin isassun tafkunan ruwa ne ya jawo tsaikon da aka samu kafin dakatar da ita.
Don haka, ya yi kira ga gwamnati da masu hannu da shuni da su tallafawa wajen samar da rijiyoyin ruwa a yankin.