Saurari premier Radio
26.9 C
Kano
Wednesday, May 1, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabarai'Yan bindiga sun kai hari kan jami'an immigration a Jigawa

‘Yan bindiga sun kai hari kan jami’an immigration a Jigawa

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan jami’an hukumar shige da fice a karamar hukumar Birniwa da ke jihar Jigawa.

Shugaban hukumar reshen jihar, ACG Ismail Abba Aliyu, ne ya bayyana hakan ya yin taron maneman labarai a Dutsen jihar Jigawa.

ya ce  ‘yan bindigar sun kashe jami’insu guda daya sannan suka jikkata mutum biyu.

Ya yi ikirarin cewa maharan sun yi wa ma’aikatansa kwanton-bauna a yayin da suke sintiri a hanyar Galadi zuwa Birniwa.

A cewarsa, ‘yan bindigar, wadanda suka kai biyar, sun isa wurin da ma’aikatan shige da ficen ke aiki ne a kan babura sannan suka bude musu wuta.

ACG Aliyu ya bayyana cewa jami’in da aka kashe shi ne Abdullahi Mohammed, yana mai karawa da cewa jami’an da aka jikkata su ne Abba Musa Kiyawa da Zubairu Garba.

Latest stories

Netanyahu ya nanata ƙudirin sojojin Isra’ila na kai farmaki ta ƙasa a Rafah.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya nanata kudirin sojojin Isra'ila...

NiMet ta yi hasashen samun mamakon ruwan sama a wasu jihohin.

Wani has ashen hukumar Kula da Yanayi ta kasa...

Related stories

Netanyahu ya nanata ƙudirin sojojin Isra’ila na kai farmaki ta ƙasa a Rafah.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya nanata kudirin sojojin Isra'ila...

NiMet ta yi hasashen samun mamakon ruwan sama a wasu jihohin.

Wani has ashen hukumar Kula da Yanayi ta kasa...