Akalla malaman jami’o’in kasar nan 20 ne suka rasa rayukansu bayan sun shiga kunci na rashin albashi sakamakon yajin aikin da jami’o’in me yi.
Kusan watanni 7 kenan da gwamnatin kasar nan ta daina biyan malaman jami’o’in albashinsu, tana mai cewa, ‘babu aiki babu albashi’
Wasu daga cikin malaman sun shaida wa sashan Hausa na RFI cewa, lallai sun yi rashin mambobinsu saboda damuwar da suka shiga.
Wannan kuwa na faruwa ne sakamakon malaman sun dogara ne kacokan kan albashin.
Laakari da ce hanya daya tilo kenan da suke samun kudaden ciyar da iyali.