Saurari premier Radio
28.9 C
Kano
Saturday, May 4, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiHajj: Rukunin farko na Alhazan Kano sun dawo gida

Hajj: Rukunin farko na Alhazan Kano sun dawo gida

Date:

Ahmad Hamisu Gwale

Rukunin farko na Mahajjatan Kano 259 sun dawo Kano daga kasa mai tsarki bayan sauke faralin a bana.

Mahajjatan kanan hukumomin Rano, Bunkure da Kura ne dai jirgin farko da hukumar jin dadin alhazai ta kasa tayi jigilar su zuwa nan Kano a ranar Juma’ar nan.

Alhazan da suka hau jirgin AZMAN mai lamba ZQ2349 sun isa filin jirgin saman Malam Aminu Kano da misalin karfe 02:41 na rana.

Babban Sakataren Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Muhammed Abba-Danbatta ne ya bayyana hakan ga manema labarai.

Muhammad Abba Danbatta ya ce  alhazan sun kasance masu biyayya da bin doka a kasa mai tsarki.

Ya ce  ana sa ran dawowar kashi na biyu na maniyyata nan gaba kadan.

Latest stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Muna duba batun mafi karancin albashi-Gwamnoni.

Kungiyar gwamnonin kasar nan, ta ce kawo yanzu tuni...

Related stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Muna duba batun mafi karancin albashi-Gwamnoni.

Kungiyar gwamnonin kasar nan, ta ce kawo yanzu tuni...