Saurari premier Radio
31.9 C
Kano
Saturday, May 4, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamnatin tarayya za ta karasa aikin titin Kano zuwa Katsina

Gwamnatin tarayya za ta karasa aikin titin Kano zuwa Katsina

Date:

Majalisar zartarwa ta kasa ta amince da fitar da karin naira miliyan dubu 16 domin karasa aikin fadada babbar hanyar Kano zuwa Katsina

Ministan yada labarai Alhaji Lai Muhammad ne ya bayyana hakan, yayin ganawa da manema labarai ranar alhamis.

Amicewar ta biyo bayan gabatar da kundin aikin fadada titin na Kano zuwa Katsina, mai nisan kilomita 78, wadda aka fara aikinta tun a shekarar 2019.

Bayan da dan kwangilar dake yin aikin ya gabatar da wani bangare na aikin ga gwamnati, kuma gwamnati ta gamsu da aikin ne yasa ta ta kara masa kudi domin ci gaba da aikin.

Haka kuma, ya nemi gwamnati ta duba tsadar kayan ayyuka a yanzu ta kara kudi domin gaggauta karasa aikin.

A don haka ne gwamnatin ta kara naira biliyan 16, inda jumlar kudin aikin ya kasance naira biliyan 46, maimakon biliyan 29 da aka ware tunda fari.

Latest stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Muna duba batun mafi karancin albashi-Gwamnoni.

Kungiyar gwamnonin kasar nan, ta ce kawo yanzu tuni...

Related stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Muna duba batun mafi karancin albashi-Gwamnoni.

Kungiyar gwamnonin kasar nan, ta ce kawo yanzu tuni...