Daga Ahmad Hamisu Gwale
Yan wasan kwallon guragu na Kano Pillars, sun kai wasan karshe a gasar Para-Soccoer bayan doke yan wasan Plateau da ci 3-2 a yammacin ranar Litinin a ci gaba da buga gasar cin kofin masu bukata tamusamman ta kasa.
Wakilinmu Ahmad Hamisu Gwale ya bamu rahotan gasar na ci gaba da gudana a filin wasa na Moshood Abioloa dake birnin Tarayya Abuja.
Tin da fari yan wasan birnin Tarayya Abuja sun yi nasarar doke yan wasan Kaduna da ci 1-0 da hakan ya basu damar kaiwa wasa karshe a gasar.
Yanzu haka yan wasan Kano Pillars na fara Para-Soccer zasu kece raini da yan wasan birnin Tarayya a wasan da zai gudana a Wannan Talatar.
Gasar cin kofin masu bukata tamusamman ta kasa ta Wannan shekarar ma’aikatar matasa da wasanni ta kasa ce ke daukar nauyin shiryawa masu bukata tamusamman domin suji ana damawa da su a harkokin wasanni.
Akalla wasanni 15 daban-daban ne ake ci gaba fafatawa a gasar cin kofin masu bukata tamusamman ta kasa dake gudana filin wasa na Moshood Abioloa dake birnin Tarayya Abuja.