Uwargidan Shugaban kasa, Aisha Buhari ta roki a hada karfi da karfe don ganin an kawo karshen rikicin da ke wakana a kasar Sudan.
Jaridar Premium Times ta ruwaito Aisha Buhari na wannan kira a wani taro da ta jagoranta a makon da muke ciki a Fadar Gwamnati da ke Abuja.
A cewar jaridar, Aisha Buhari na ganin akwai rawar da matan shugabannin Afirka za su iya takawa musamman wajen kai agaji Sudan.
Tun ranar 15 ga watan Afrilu, yaki ya barke a Sudan kuma har wannan lokaci, an kasa cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta dindindin.
Sama da mutane 500 ake kyautata zaton cewa rikicin ya yi sanadin rasuwarsu kawo yanzu.