Abdulrashid Hussain
Najeriya za ta fara karbar haraji daga masu amfani da kundin Internet na crypto currency.
Ministar kudi, kasafi da tsare-tsare, Zainab Ahmad, ta sanar da shirin gwamnati na sanya haraji kan kudaden internet na crypto currency da sauran hada-hadar kudi a cikin kudirin sake fasalin dokokin kudi na 2023.
Ministar ta bayyana haka ne yayin taron majalisar tattalin arziki ta tarayya da mataimakin shugaban kasa farfesa Yemi Osinbajo ya jagoranta.
A wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin shugaban kasa Laolu Akande ya fitar, yace ministar kudin ta bayyanawa majalisar abunda kudirin karbar harajin ya kunsa.
Tace tsarin dokokin da ake son gabatarwa zasu samar da ayyukan yi, habakar tattalin arziki, da kuma sake fasalin yadda ake samun kudin shiga da yadda ake tassarufi da su.
Wannan dai na zuwa ne bayan shafe sama da shekara daya da matakin gwamnatin tarayya na haramta kasuwanci kudin internet din na crypto currency.
Abunda yasa masu gudanar da hada-hadar kudin internet din suka bayyana karbar harajin daga garesu a matsayin alamun za’a maido da hallacin kasuwancin nasa.