Hafsat Nasir Umar
Hukumar Zabe mai zaman kanta ta sanar da ranakun da za ta rabar da katinan zabe a fadin kasar.
A wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na Tuwita ta ce ta saka ranakun Litinin 12 ga watan Disamba zuwa Lahadi 22 ga watan Janairun 2023 a matsayin ranakun da za ta rabar da katinan zaben a ofisoshinta da ke fadin kananan hukumomin kasar 774.
Tuni dai hukumar ta sanar da ranar 25 ga watan Fabrairun 2023 a matsayin ranar da za ta gudanar da zaben shugaban kasar tare da na ‘yan majalisun dokoki.
Yayin da za a gudanar da zaben gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi ranar 11 ga watan Maris din 2023.