Saurari premier Radio
30.9 C
Kano
Saturday, April 20, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamnatin KanoMajalisa ta kammala tantance kwamishinonin da Gwamnan Kano ya aike mata

Majalisa ta kammala tantance kwamishinonin da Gwamnan Kano ya aike mata

Date:

Aminu Abdullahi Ibrahim

 

Majalisar dokokin Kano ta tantance tare da amincewa da nadin Aminu Ibrahim Tsanyawa, a matsayin kwamishina kuma mamba a majalisar zartaswa ta jihar Kano.

 

Majalisar ta amince da shine a zamanta na Ranar Talatar karkashin jagorancin shugaban majalisar Injiniya Hamisu Ibrahim Chidari.

 

A zaman majalisar na jiya Litinin ne gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya aike da sunan Aminu Ibrahim Tsanyawa, don tantance shi cikin mutane goma da za a nada kwamishinoni don maye gurbin wadanda suka ajiye aiki domin yin takara a zaben badi dake tafe.

 

Aminu Ibrahim Tsanyawa dai shine tsohon kwamishinan lafiya da ya sauka don shiga zaben fidda gwani, inda ya nemi takarar majalisar tarayya mai wakiltar kunci da Tsanyawa.

 

Sai dai rashin samun tikitin takarar yasa kuma gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya sake tura sunan sa don nada shi a matsayin kwamishina, wanda kuma majalisar ta amince dashi a zamanta na Talatar nan.

 

Da yake jawabi bayan tantance shi Aminu Ibrahim Tsanyawa, ya ce zai dora kan ayyukan ci gaba da ya faro don ciyar da jihar Kano gaba.

 

Aminu Ibrahim Tsanyawa, ya kuma ce wannan karon zasu fi maida hankalin ga bangarorin da suka fi fuskantar matsala domin magance su.

Latest stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...