Kungiyoyin kwadagon kasarnan NLC da TUC da kuma kungiyar tuntuba ta masu daukan ma’aikata, NECA, sun koka kan yadda ake ci gaba da samun faduwar darajar Naira, inda suka bukaci gwamnatin tarayya da ta dauki matakin gaggawa na daidaita lamarin.
Kungiyar ta NLC ta yi gargadin cewa idan ba a yi gaggawar daukar matakan da suka dace don tilastawa hukumomin da abin ya shafa ba wajen ceto darajar naira to hakan zai kara rusa tattalin arzikin kasar da kuma al’umar kasar baki daya.
A yayin da ita kuma kungiyar ta TUC ta bayyana damuwa kan illar da faduwar darajar Naira ke yi ga ma’aikata, ta hanyar hauhawar farashin kayayyaki, ita ma kungiyar NECA, wadda ita ce muryar kasuwanci a Najeriya, ta koka kan yadda faduwar darajar Nairar ya sa durkushewar kasuwanci a kasar.
Daga bisani kungiyoyin sun bukaci gwamnatin tarayya da ta shawo kan matsalolin da suka kawo faduwar darajar nairar domin magance matsalar hauhawar farashi da ake fuskanta a kasar.
Kungiyoyin kwadagon kasarnan NLC , TUC da NECA sun koka kan yadda ake ci gaba da samun faduwar darajar Naira
Date: