Karibullah Abdulhamid Namadobi
Sabon shugaban kungiyar daliban Jami’ar Yusuf Maitama Sule Tafida Akilu ya ce zasu yi kokari wajen tsaftace siyasar dalibai tare da gyara alakar dake tsakanin malamai da dalibai.
Tafida Akilu ya bayyana hakan ne yayin tattaunawar sa da Premier Radio bayan ya zama shugaban daliban jami’ar.
Tafida Akilu ya ce a wannan karon ba a gudanar da zabe ba yayin samar da shugabbannin daliban kasancewar hukumar jami’ar ta yi maslaha a tsakanin ‘yan takara, wanda hakan ya ba shi damar kasancewa shugaban kungiyar.
Ya kara da cewa zasu fito da sabbin tsare-tsare wajen ganin sun taimakawa dalibai ta bangaren koyo da koyarwa.
Sabon shugaban kungiyar daliban Jami’ar Yusuf Maitama Sule, Tafida Akilu ya bukaci dalibai su bashi hadin kai domin gudanar da shugabanci cikin nasara.