Saurari premier Radio
25.1 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiKiwon LafiyaGwamnatin Tarayya Zata Rufe Dakunan gwaje-gwajen Da Basu Da Rajista

Gwamnatin Tarayya Zata Rufe Dakunan gwaje-gwajen Da Basu Da Rajista

Date:

Gwamnatin tarayyar na shirin rufe dakunan gwaje-gwajen da ba a yiwa rajista ba a kasar don tsaftace fannin kiwon lafiya.

 

Karamin Ministan Lafiya, Joseph Ekumamankama ya bayyana haka yayin da ya bukaci mahukunta da ma’aikatan kungiyar kimiyyar dakin gwaje-gwajen lafiya ta Najeriya da kada su yi kasa a gwiwa wajen gudanar da ayyukansu bisa tsarin doka.

 

Ya yi wannan bayani ne a lokacin da mambobin ƙungiyar karkashin jagorancin magatakardar, Dokta Tosan Erhabor suka kai masa ziyarar ban girma a hedikwatar ma’aikatar lafiya da ke Abuja.

 

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar lafiya ta fitar a ranar Asabar ta hannun Daraktan yada labarai, Ahmed Chindaya, ministan ya bayyana cewa za a samar da tsare-tsare don tabbatar da gudanar da harkokin ƙungiyar cikin sauki.

 

Ya ce, idan akwai bukata, za a samar da tsare-tsare da za su taimaka wajen gudanar da ayyukansu, yadda ya kamata, domin cimma wa’adin da shugaban kasa ya dora a bangaren kiwon lafiya.

 

Ministan ya bada tabbacin asibitocin da ke karkashin ma’aikatar lafiya ta tarayya za su kasance farkon asibitocin da za su fara aiwatar da cikakken tanade-tanaden dokar, daganan kuma dakunan gwaje-gwaje a asibitocin jihar za su biyo baya. Da zarar an kammala hakan in ji ministan, za a rufe dakunan gwaje-gwajen likitocin da ba su yi rajista da MLSCN ba.

 

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...