Daga Qaribullah Abdulhamid Namadobi
Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje yayi Allah wadai da lalata motar kungiyar kwallon kafa ta Katsina United a yayin da kungiyar kwallon kafa ta Kano pillars ta karbi bakuncinta a filin wasa na Sani Abacha dake Kano.
Kano Pillars za ta dawo Kano da buga wasa
Gwamna Ganduje yace zasu kafa kwamiti mai karfi don binciko musabbabin hatsaniyar da ta faru a wasan da Kano Pillars tayi da Katsina United a makon da ya gabata.
A cikin wata sanarwa da sakataran yada labaran gwamna Abba Anwar ya fitar ya ce gwamnatin Kano zata siyawa Katsina United sabuwar mota.