33.9 C
Kano
Sunday, June 4, 2023
HomeLabaraiSaudiyya ta baiwa Najeria mutum dubu 43 da za su sauke farali...

Saudiyya ta baiwa Najeria mutum dubu 43 da za su sauke farali a bana

Date:

Related stories

Maniyyata 17,000 ne suka bar Najeriya zuwa kasa maitsarki-NAHCON

Bayan kwashe kwanaki bakwai da fara jigilar alhazan Najeriya...

Mukhtar Yahya Usman

Hukumomin a kasar saudiyya sun baiwa kasar nan adadin mutun 43,000 da za su sauke farali a bana.

Babban sakataren hukumar Jin dadin alhazai na Kano Muhammad Abba Danbatta ne ya sanar da hakan yayin taron manema Labarai ranar Laraba.

Danbatta ya ce wannan ya biyo bayan yadda kasar ta Saudiyya ta ce adadin mutun Milyan daya ne kawai za su gudanar da aikin hajjin bana a fadin duniya.

Ya ce wannan adadi da aka baiwa Najeria na da alaka da yawan mutanen da Najeria ta ke da shi.

Muhammad Danbatta ya ce ko dayake har yanzu NAHCON bata fitar da kudin aikin hajjin bana ba Amma alamu na nuna kudin zai karu.

Ya ce a baya an canja Dala akan 350 yanzu kuma ta Kai 408 da ke nuna lallai za a samu Karin kudin.

A yanzu dai ana jihar hukumar Jin dadin alhazai ta kasa ta baiwa kowacce jiha adadin kujerunta tare da bayyana adadin kudin na bana.

Latest stories