Saurari premier Radio
23.8 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeKwaryar KiraFashewar Tukunyar Gas: Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta Kafa Kwamatin Bincike

Fashewar Tukunyar Gas: Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta Kafa Kwamatin Bincike

Date:

Abdurrashid Hussain

Majalisar dokokin Jihar Jigawa ta kafa kwamati da zai gudanar da bincike domin gano musabbabin fashewar tukunyoyin iskar gas din da ta faru a Karamar Hukumar Babura.

 

Shugaban Majalisar Alhaji Garba Idris Jahun ya bayyana haka yayin zaman majalisar na jiya alhamis.

 

Ya bayyana sunan mataimakin bulaliyar majalisar Barista Bala Hamza Gada, a matsayin shugaban kwamatin sai kuma yan majalisar dake wakiltar kananan hukumomin Dutse da Kiyawa da Miga da Babura a matsayin mammbobi.

 

Haka kuma Majalisar ta bayyana damuwa kan barnar da ambaliyyar ruwa tayi a sassan jihar ta Jigawa, inda ta nemi gwamnati ta taimakawa wadanda iftila’in ya shafa.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories