Abdurrashid Hussain
Majalisar dokokin Jihar Jigawa ta kafa kwamati da zai gudanar da bincike domin gano musabbabin fashewar tukunyoyin iskar gas din da ta faru a Karamar Hukumar Babura.
Shugaban Majalisar Alhaji Garba Idris Jahun ya bayyana haka yayin zaman majalisar na jiya alhamis.
Ya bayyana sunan mataimakin bulaliyar majalisar Barista Bala Hamza Gada, a matsayin shugaban kwamatin sai kuma yan majalisar dake wakiltar kananan hukumomin Dutse da Kiyawa da Miga da Babura a matsayin mammbobi.
Haka kuma Majalisar ta bayyana damuwa kan barnar da ambaliyyar ruwa tayi a sassan jihar ta Jigawa, inda ta nemi gwamnati ta taimakawa wadanda iftila’in ya shafa.