Saurari premier Radio
41.8 C
Kano
Wednesday, May 1, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiBinani ce zata zama gwamna mace ta farko da za a zaba...

Binani ce zata zama gwamna mace ta farko da za a zaba Najeriya –Buhari

Date:

Hafsat Nasir Umar

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce Sanata Aisha Ahmed Binani, zata kasance gwamna mace ta farko da zata yi nasara a zaben kasar nan.

 

Ya bayyana haka ne a ranar  litinin din nan yayin da ya kai ziyara fadar Lamidon Adamawa da ke Yola.

 

Buhari da sauran jiga-jigan jam’iyyar ciki harda dan takarar shugaban kasa na APC Bola Ahmad Tinubu, sun kai ziyara jihar ne jihar domin gudanar da yakin neman zaben ‘yar takarar gwamnan.

 

Buhari ya ce idan aka zabi Binani a matsayin gwamna hakan zai samar da damarmaki ga mata a kasar nan.

 

Ya ce zai cigaba da bata goyon bayan da take bukata domin samun nasara.

 

Latest stories

Related stories