Hafsat Nasir Umar
Direbobin tankar da suka tare hanyar Zariya zuwa Kano bayan wani soja ya halaka guda daga cikin direbobin sun saki hanya.
A Asabar din nan, direbobin suka amince su janye motocin nasu da suka tare hanyar bayan tattaunawa da jami’an tsaro da kuma jami’an Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC).
Lamarin dai ya haifar da cunkoson ababen hawa tsawon kwanaki, inda mutane suka koma amfani da wasu hanyoyin, wasu kuma da dama suka yi curko-curko.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin mai rikon mukamin Kwamandan FRSC na Jihar Kaduna, Lawal Garba, ya ce yanzu lamura sun daidaita a hanyar.
Tuni Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna ta sanar da kaddamar da cikakken bincike kan kisan da sojan yayiwa direban, wanda shi ne ya haddasa rufe hanyar tun da farko.