Saurari premier Radio
29.9 C
Kano
Saturday, May 4, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiMuna so a hukunta dan uwanmu da ya kashe Ummita-‘Yan China mazauna...

Muna so a hukunta dan uwanmu da ya kashe Ummita-‘Yan China mazauna Kano

Date:

Mukhtar Yahya Usman

 

Al’ummar China mazauna Kano sun bukaci a hukunta dan kasarsu da ake zargi da kisan wata mata ‘yar Kano mai suna Ummukulsun Buhari  a unguwar Jambulo.

 

Wannan na kunshe cikin wata samarsa da Wakilin Mutanen China a Kano Mike Zhang ya fitar ranar Litinin a Kano.

 

Sanarwar ta yi Allah wadai da kisan matashiyar, kuma ta bukaci a hukunta shi dai-dai da abinda ya aikata.

 

Haka zalika ta bukaci mahukunta su gudanar da binciken kwakwafi kan lamari daga dukkanin bangarorin jami’an tsaro.

 

Sanarwar ta ce al’ummar China a Kano na bin dukkanin dokokin kasa kuma suna bin duk dokar da aka gindaya musu.

 

Su kuma nuna jin dadinsu kan irin damar da aka basu suke zaune a Kano ba tare da takuraba.

 

Al’ummar ta kuma mika sakon ta’aziyyarta ga iyalai da dangin mamaciyar inda suka roki Allah ya gafarta mata.

 

Latest stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Muna duba batun mafi karancin albashi-Gwamnoni.

Kungiyar gwamnonin kasar nan, ta ce kawo yanzu tuni...

Related stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Muna duba batun mafi karancin albashi-Gwamnoni.

Kungiyar gwamnonin kasar nan, ta ce kawo yanzu tuni...