Saurari premier Radio
35.9 C
Kano
Sunday, May 5, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiDa Dumi-dumiƳan sandan Jamus sun kama ƴan Najeriya 11 bisa zargin ƙungiyar asiri...

Ƴan sandan Jamus sun kama ƴan Najeriya 11 bisa zargin ƙungiyar asiri da soyayyar ƙarya don yaudara

Date:

Ƴan sandan Jamus sun kama ƴan Najeriya 11 da ake zargin ƴan ƙungiyar asiri ne da suke shirya soyayyar ƙarya don yaudara.

A wata sanarwa da ƴan sandan Bavarian suka fitar, ƴan ƙungiyar asirin ta Black Axe sun aikata manyan laifuka da dama a faɗin duniya.

Ƴan sandan sun ƙara da cewa ƙungiyar ta mayar da hankali kan ƙulla soyayyar ƙarya da kuma halasta kuɗin haram a Jamus.

Sanarwar ta ce, suna yin ɓadda kama, misali suna zuwa da niyyar aure sannan bayan an ɗau wani lokaci ana soyayyar sai su nemi a basu kuɗaɗen yin wasu ɓukatu.

Ɓangarorin da ƙungiyar take aiki a faɗin duniya sun haɗa da safarar bil’adama da yaudara da halasta kuɗin haram da safarar miyagun ƙwayoyi.

Waɗanda aka kama ɗin duka ƴan Najeriya ne kuma ƴan shekaru tsakanin 29 da 53.

An tsare su a ranar Talata a sumamen da aka kai yankin Bavaria bayan binciken ƴan sanda da aka shafe sama da shekara biyu ana yi.

Latest stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...

Related stories

2023 ita ce shekara mafi muni ga yan jarida.

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan'adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta...