Saurari premier Radio
32.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabarai'Yan sanda sun kama barayin da suka saci takalmi a Ekiti

‘Yan sanda sun kama barayin da suka saci takalmi a Ekiti

Date:

‘Yan sanda a jihar Ekiti sun kama mutum biyu Olamide da Michael kan zargin sata takalma da fasa gidaje 16 da kantina a Ado Ekiti babban birnin jihar.

 

Wannan na kunshe cikin wata sanarwar da jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan jihar Sunday Abutu, ya fitar ranar Litinin.

 

Sanarwar ta ce kama Olamide da aka yi ne ya kai su ga kamo Michael, an kuma yi nasarar gano kayayyakin da suka sata a gidajen mutanen da suka kai korafin anyi musu sata.

 

A cewar sanarwar an samu kayan lantarki daban daban da takalma na maza da mata 220 a  maboyar baryin.

 

Haka kuma an samu kayan sawa na maza da mata 275 da barasa masu tsada da kayan masarufi da dai sauran abubuwa.

 

Sunday Abutu ya kara da cewa, “ya yin da ake ta kokarin kama wadanda suka tsere ne aka gano wadannan kayan, kuma da zarar an kammala bincike za a gurfanar da su gaban shari’a.

 

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...