Hukumomin Saudiyya sun ce za a gabatar da Sallar Kisfewar Rana a Masallacin Harami yau Talata.
Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da shafin Facebook na Haramain Sharifain ya wallafa ranar Litinin.
Tun a makon da ya gabata, aka samu rahoton za a samu kisfewar rana a wasu ƙasashen duniya ciki har da Saudiyya.
“Wanda zai jagoranci Sallar Kisfewar Rana a Masallacin Harami a yau (Talata) shi ne Sheikh Bandar Baleelah.
Yayin da Sheikh Ahmad Huzaify zai jagoranci Sallar a Masallacin Madina.
Za a gudanar da Sallar ne da misalin karfe 1:45 na rana dai DAI da 4:45 agogon Najeriya.
Musulunci ya sunnanta cewa duk lokacin da aka samu kisfewar rana ko wata to Musulmi su yi sallar nafila da nufin neman sauki daga Ubangiji Madaukakin Sarki.
A wani hadisi, Manzon Allah (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) ya ce: “Haƙiƙa rana da wata ayoyi ne daga cikin ayoyin Allah. Ba sa kisfewa saboda mutuwar wani ko saboda rayuwarsa”.