Daga Ahmad Hamisu Gwale
A wannan rana ta Talata, shida ga Satumbar shekarar da muke ciki, za a fara gasar cin kofin zakarun nahiyar turai ta kakar wasannin shekarar 2022/2023.
Gasar wadda Kungiyoyi 32 zasu fafata daga sassa daban-daban na kasashen nahiyar turai, da ake saran Fara wasannin rukuni daga shida ga Satumba, zuwa biyu ga Nuwambar da muke ciki kwanaki kadan kafin fara gasar cin kofin duniya a Qatar.
Yayinda kuma wasannin kwaf daya zasu gudana a ranar 14 ga Fabrairun shekara mai zuwa, inda kuma a buga a wasan karshe na gasar a ranar 10 ga Yunin 2023 a birnin Istanbul na kasar Turkiyya.
Wasan farko na matakin rukuni zasu fara daga a wannan rana ta shida ga watan na Satumba sun hada………
Dinamo Zagreb da Chelsea da karfe (18:45)
Borrussia Dortmund da Copenhagen da karfe (18:45)
Salzburg da AC Milan da karfe (21:00)
Celtic da Real Madrid da karfe (21:00)
Leipzig da Shakhtar (21:00)
Sevilla da Man City (21:00)
Paris da Juventus (21:00)
Benfica da Maccabi Haifa(21:00)
A kakar wasannin da ta gabata dai kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ce ta lashe gasar, bayan doke Liverpool da ci 1-0 a wasan karshen da suka fafata