Saurari premier Radio
28.9 C
Kano
Friday, May 17, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiWasanniWasannin da zasu gudana a kofin duniya a wannan Juma ar

Wasannin da zasu gudana a kofin duniya a wannan Juma ar

Date:

Bayan hutun kwanaki biyu a gasar cin kofin duniya da ke gudana a Qatar.

 

A wannan rana ta Juma’a 9 ga Disambar da muke ciki, za a ci gaba da fafata gasar ta shekarar 2022.

 

Zagayen dab dana kusa da karshe a gasar za a ci gaba a yammaci da kuma daren wanann Juma ar.

 

Kasar Crotia wadda tayi rashin nasara a wasan karshe a shekarar 2018 zata kece raini da Brazil da ta fi kowacce kasa lashe wannan gasa.

 

Wasan zai gudana da karfe 4 a filin Education City Stadium, karkashin jagorancin Michael Oliver dan kasar Ingila.

 

Haka zalika itama kasar Netherlands wadda a shekarar 2012 tayi rashin nasara a hannun Sifaniya, zata barje gumi da Argentina da itama a shekarar 2014 taji babu dadi da ci 1-0 a hannun Jamus.

 

Wasa tsakanin kasashen biyun zai gudana da karfe 8 na dare, a katafaren filin wasa na Lusail wanda nan ne za a buga wasan karshe a wannan gasa.

 

Kuma ana saran Dan kasar Sifaniya Antonio Mateu Lahoz shi ne zai jagoranci fafatawar .

 

Abin jira a gani shi ne kowacce kasa ce zata kai wasan kusa da karshe a wannan gasa ta shekarar 2022 da ke gudana a Qatar.

Latest stories

Kananan Hukumomi 14 A Kano Na Fuskantar Barazanar Ambaliya A Bana

Mukhtar Yahya Usman Hukumar kula da yanayı ta kasa NİMET...

Related stories

Kano Pillars ta dakatar da mai horas da ƴan wasanta nan take.

Hukumar gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta...

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...