Bayan hutun kwanaki biyu a gasar cin kofin duniya da ke gudana a Qatar.
A wannan rana ta Juma’a 9 ga Disambar da muke ciki, za a ci gaba da fafata gasar ta shekarar 2022.
Zagayen dab dana kusa da karshe a gasar za a ci gaba a yammaci da kuma daren wanann Juma ar.
Kasar Crotia wadda tayi rashin nasara a wasan karshe a shekarar 2018 zata kece raini da Brazil da ta fi kowacce kasa lashe wannan gasa.
Wasan zai gudana da karfe 4 a filin Education City Stadium, karkashin jagorancin Michael Oliver dan kasar Ingila.
Haka zalika itama kasar Netherlands wadda a shekarar 2012 tayi rashin nasara a hannun Sifaniya, zata barje gumi da Argentina da itama a shekarar 2014 taji babu dadi da ci 1-0 a hannun Jamus.
Wasa tsakanin kasashen biyun zai gudana da karfe 8 na dare, a katafaren filin wasa na Lusail wanda nan ne za a buga wasan karshe a wannan gasa.
Kuma ana saran Dan kasar Sifaniya Antonio Mateu Lahoz shi ne zai jagoranci fafatawar .
Abin jira a gani shi ne kowacce kasa ce zata kai wasan kusa da karshe a wannan gasa ta shekarar 2022 da ke gudana a Qatar.